“A Shirye Muke Mu Koma Jam’iyyar APC… Idan an amince da sharuddanmu” – In ji Kwankwaso

IMG 20250920 WA0034

Daga Aminu Bala Madobi

Jagoran jam’iyyar NNPP na kasa, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, ya bayyana wasu sharudda na musamman da zai yi tunanin komawa jam’iyyar APC, inda ya jaddada cewa duk wani kawancen siyasa dole ne ya mutunta muradun tafiyarsa ta Kwankwasiyya.

Tsohon dan takarar shugaban kasa, Kwankwaso, ya bayyana hakan ne a lokacin da yake karbar tsohon mai baiwa tsohon gwamna Abdullahi Ganduje shawara kan harkokin siyasa, Buhari Bakwana, tare da ‘yan jam’iyyar APC da suka fito daga kananan hukumomin jihar 44 a gidansa da ke Kano.

“Ni a shirye nake in shiga jam’iyyar APC, amma a karkashin wata yarjejeniya da zata tabbatar da cikakkiyar tafiyar siyasara ta Kwankwasiyya.

“Motsina da jama’ata su ne abu mafi muhimmanci a gare ni, kuma ba zan iya watsi da su ba saboda sune idona na siyasa,” in ji Kwankwaso.

Kwankwaso ya yi tsokaci kan rawar da ya taka wajen kafa jam’iyyar APC, inda ya nuna rashin jin dadinsa kan yadda aka yi da shi da abokansa a tsawon shekaru takwas da jam’iyyar ta yi karkashin tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari.

“Muna cikin wadanda suka kafa jam’iyyar APC kuma mun sha fama da gallazawa daga jami’an tsaro daban-daban yayin da muke kalubalantar gwamnatin da ta shude.

“Duk da haka lokacin da jam’iyyar ta karbi mulki, ba mu sami wani yabo,.jinjina ko godiya kan sadaukarwar da muka yi ba, kawai saboda ba mu fito daga bangarensu na asali ba,” in ji shi.

Ya kuma soki jam’iyyar PDP da irin wannan cin zarafi a lokacin da kungiyarsa ta yi yunkurin komawa jam’iyyar, inda ya ce ba su ma iya ba shi mukamin shugaban jam’iyyar na shiyyar. Wannan gogewa, in ji shi, ya ƙarfafa yunƙurinsa na samun ‘yanci a siyasa.

Ya ci gaba da cewa “A shirye muke mu koma jam’iyyar APC a karkashin wani sharadi mai karfi da kuma alkawuran da muka dauka.

Dan takarar shugaban kasa har sau biyu ya jaddada cewa tsarin siyasar sa ya rikide zuwa wani tarago mai karfi a siyasar Najeriya wanda ba za a manta da shi ba, yana mai jaddada cewa sun gamsu a cikin jam’iyyar NNPP kuma ba su da burin ficewa cikin gaggawa. “Duk da haka, muna ci gaba da kasancewa a shirye don haɗin gwiwa na gaske tare da duk wani ɓangaren da ke son mutunta yarjejeniyar mu tare da ɗaukar mu a matsayin abokan hulɗa na bai ɗaya.”

A karshe Sanata Kwankwaso ya ce ko da jam’iyyar adawa ta PDP za ta tunkare shi da amincewa da kura-kuran su na baya, a shirye yake da duk wani hadin gwiwa da za a yi kuma ya zama wajibi a dauki kwararan matakai a bayyane a bainar jama’a.

Ga masu son bada talla ko shawarwari a kira wannan lambar +2348032077835

Domin samun sauran shirye-shirye Alfijir labarai/Alfijir news ku biyo mu ta nan 👇

https://twitter.com/Musabestseller?s=09

https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165

https://www.threads.net/@alfijirlabarai

https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12

https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag

Alfijir labarai Alfijir News Whatsapp Group 👇👇

https://chat.whatsapp.com/H5oBRaZBdCVIyOTIV5eMfb?mode=ac_t

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *