Bankada! Bayan cire tallafin man fetur mun ninka kuɗaɗen da mu ke baiwa jihohi sau uku – Tinubu

IMG 20250212 WA0210

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya ce cire tallafin man fetur ya sa gwamnatinsa ta ninka kuɗaɗen da take bai wa jihohi daga asusun tarayya sau uku.

Alfijir labarai ta rawaito cewa da yake magana yayin taron shugabannin jam’iyyarsu ta APC a Abuja ranar Talata da dare, Tinubu ya lissafa abubuwan da ya ce cire tallafin ya bai wa gwamnatinsa damar yi.

“Babu ta yadda za a yi Najeriya ta ɗore matuƙar ba a daina biyan tallafin [man fetur] ba,” in ji shi.

“Mun ninka kaso na kuɗin da jihohi ke samu sau uku. Muna da isassun kuɗin da za mu bai wa ƙananan hukumomi. Mun kafa hukumar Nelfund da za ta dinga biyan kuɗin karatun ‘ya’yanmu.

“Za mu iya saita makomar ƙasar nan. Abubuwan da ke faruwa a duniya na burge ni, ba don komai ba sai yadda suke koya mana darasi cewa mu ‘yan Najeriya za mu iya gina kanmu kuma mu taimaka wa Afirka ta ci gaba.”

Matashiya: Shugaba Tinubu ya cire tallafin man fetur a watan Mayun 2023, wanda ya sa farashinsa ya tashi daga ƙasa da N200 zuwa sama da N1,000 a yanzu.

BBC

For more information about  Alfijir labarai/Alfijir news follow here  👇

https://twitter.com/Musabestseller?s=09

https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165

https://www.threads.net/@alfijirlabarai

https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12

https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag

Alfijir labarai Alfijir News Whatsapp Group 👇👇

https://chat.whatsapp.com/IqPyC2oGzdQ9NudcMXFqHZ

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *