ECOWAS Sun Mai Da Martani Mai Zafi Kan Abdourahmane Tchiani

Kungiyar Raya Tattalin Arzikin Kasashen Yammacin Afirka ECOWAS ta ce ba za ta amince sojoji su ci gaba da rike mulkin Nijar ba har nan da shekaru uku masu zuwa.

ECOWAS na wannan batu a matsayin martani da maganar da shugaban mulkin sojin Nijar ya yi na cewa zai mayar da ƙasar kan tafarkin dimokuradiyya cikin shekara uku masu zuwa.

Cikin wata sanarwa da shugaban mulkin sojin ƙasar, Janar Abdourahmane Tchiani ya fitar da maraicen ranar Asabar, ya ce zai miƙa mulki hannun farar hula cikin shekara uku.

A tattaunawarsa da BBC, kwamishinan harkokin siyasa da tsaro da tabbatar zaman lafiya na ECOWAS, Abdel-Fatau Musa, ya ce yana ganin sanarwar da Janar Tchiani ya fitar dabara ce ta buƙatar tattaunawa.

Ya ƙara da cewa ya kamata a ce jagororin sojin Nijar sun mayar da hankali wajen yaƙar ’yan ta’adda, maimakon harkokin mulkin ƙasar.

Ƙungiyar dai na buƙatar sojojin su mayar da hamɓararren shugaban ƙasar, Mohamed Bazoum kan mulki ba tare da ɓata lokaci ba.

ECOWAS ta kuma yi barazanar amfani da ƙarfin soji domin mayar da hamɓararren shugaban ƙasar Mohamed Bazoum.

To sai dai cikin sanarwar da ya fitar, ranar Asabar, Janar Tchiani ya yi gargaɗin cewar amfani da ƙarfin soji ka iya wargaza zaman lafiyar ilahirin yankin Yammacin Afirka.

Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a

Facebook.   Alfijir Labarai
YouTube.     Best Seller Channel
Twitter.        @Musabestseller
Instagram.  @musa_bestseller

Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijir Labarai  👇

https://chat.whatsapp.com/Jmw5CBsPV6H3DbSgnlFUHM

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *