Wasu ‘yan bindiga sun kai hari gidan wani malami a jami’ar tarayya ta Dutsinma (FUDMA) da ke jihar Katsina mai suna Dakta Tiri Gyan David,
Lamarin ya faru ne a Lowcost Yarima Quarters da misalin karfe 1:30 na dare a ranar Talata, 2 ga Yuli, 2024.
Alfijir labarai ta ruwaito cewa ‘yan bindigar sun kashe malamin tare da sace ‘ya’yansa guda biyu. Malamin, mai suna Dakta Tiri Gyan David, shi ne Shugaban sashen tattalin arziƙi na noma, bunƙasawa da raya Karkara a jami’ar FUDMA.
Majiyarmu ta tabbatar da cewa ‘yan ta’addan sun dira a Unguwar ne da manyan makamai tare da yin harbe-harben kan mai uwa da wabi.
Wani ganau ya shaida wa wakilinmu cewa harbe-harben da aka yi ya sa suka farka: “Mun shiga damuwa matuƙa, da misalin ƙarfe 1:35 na dare, sai muka ji ƙarar harbe-harbe ta ko’ina a Unguwar, daren ya kasance mana mai ban tsoro. Sai muka ji kuma an kashe wani malamin FUDMA, sannan an sace wasu daga cikinsu ‘ya’yansa”.
Da aka tuntuɓi Kakakin Rundunar ’Yan sandan Jihar Katsina, Aliyu Sadeeq, ya tabbatar da faruwar lamarin inda ya ce nan ba da jimawa ba za su fitar da sanarwa.
Jaridar Daily Struggle
Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a
Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijr Labarai 👇👇