Allah Ya yi wa Hajiya Zainab, matar Mataimakin Gwamnan Jihar Neja, Yakubu Garba rasuwa.
Hajiya Zainab ta rasu ne a asibiti bayan gajeruwar rashin lafiya a wani asibiti da ke Minna, babban birnin jihar a ranar Talata.
Gwamnan jihar, Mohammed Umaru Bago, ya bayyana alhini da game da wannan rashi.
Sakon ta’aziyyar da kakakinsa, Bologi Ibrahim, ya sa wa hannu ya bayyana rasuwar a matsayin babban rashi ga jihar.
Ya kuma yi addu’a Allah Ya sada ta da mafificin rahama a Aljanna Firdausi, Ya ba wa mijinta hakurin jure wannan rashi.
Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a
https://twitter.com/Musabestseller?s=09
https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165
https://www.threads.net/@alfijirlabarai
https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12
https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag
Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijr Labarai 👇👇
https://chat.whatsapp.com/ELQRQyq1zGn7zpAVP8DwNj