Rundunar Ƴan Sanda Ta Kama Mutune 3 Da Wayoyin Sata Kimanin 318 A Kano

Screenshot 20231015 001416 com.whatsapp edit 3294010975537

Dubun wasu matasa uku da rundunar yan sandan jihar Kano ta kama da wayoyin hannu 318 wadanda ake zargin na sata ne ta cika.

Alfijir Labarai ta rawaito kakakin rundunar SP Abdullahi Haruna Kiyawa ne ya bayyana haka a wani sako da ya wallafa a shafin sada zumunta ranar Asabar.

Kiyawa ya bayyana cewa tun da farko wani mai suna Muhammad Adam da wasu mutane 9 ne suka kai musu korafi kan cewa da tsakar dare barayi sun fasa musu shaguna a kusa da filin wasa na Sani Abacha dake kofar Mata Kano, inda suka sace wayoyi 671.

Nan take ‘yan sanda suka soma bincike wanda har ya kai ga kama mutanen uku, sun kuma amsa laifin da ake zargin su da aikata wa.

Sai dai wadanda ake zargin sun shaida wa ‘yan sandan cewa tuni suka sayar da wasu daga cikin wayoyin.

SP ya bayyana cewa za a gurfanar da mutunen a gaban kotu da zarar ta kammala bincike.

Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a

https://twitter.com/Musabestseller?s=09

https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165

https://www.threads.net/@alfijirlabarai

https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12

https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag

Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijir Labarai  👇

https://chat.whatsapp.com/K8z1chFesJeCf99QehWJPo

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *