Daga Aminu Bala Madobi
Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya sallami Shugaban Hukumar Alhazai ta Najeriya (NAHCON), Malam Jalal Arabi.
Alfijir labarai ta ruwaito sallamar tasa na zuwa ne bayan zargin shugaban da yin sama da fadi da wani ɓangare na naira biliyan 90 da gwamnatin Najeriya ta ba hukumar a matsayin tallafi ga aikin hajjin 2024 da ya gabata.
Wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban Ajuri Ngelale ya fitar, ta kuma tabbatar da naɗa Farfesa Abdullahi Saleh Usman a matsayin sabon shugaban hukumar ta alhazan Najeriya.
Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a
https://twitter.com/Musabestseller?s=09
https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165
https://www.threads.net/@alfijirlabarai
https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12
https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag
Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijr Labarai 👇👇
https://chat.whatsapp.com/ELQRQyq1zGn7zpAVP8DwNj