Alfijr ta rawaito kotu ta ce, ta samu Abduljabbar Kabara da laifin yiwa ma’aiki (s a.w) kage da cin mutumcin ma aiki da cewar yayi fyade ,
An same shi da laifi karkashin sashe na 382 (B)
Lauyan da ke kare shi Barrister Aminu Abubakar yace ayi masa sassauci saboda kuskuren fahimta ce tasa Malam Abduljabbar ya aikata wannan laifi.
Amma nan take malamin ya miƙe ya ce shi dai ba da yawunsa ba, Lauyana yake magana.
Malamin ya ce, baya neman sassauci, kuma yana neman a gaggauta yi masa hukunci domin zai yi mutuwa ta girma
Freedom Radio
Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a
Facebook. Best seller Channel
YouTube. Best Seller Channel
Twitter. @Musabestseller
Instagram. @musa_bestseller
Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijr Labarai 👇
Allah ya ganar damu gaskiya yakuma bamu ikon binta Ameen