Wata Kotu Ta Garkame Asusun Wani Gwamna Kan Badakalar Bashin N3.4bn

Alfijr ta rawaito wata babbar kotun birnin tarayya Abuja ta bayar da umarnin toshe kudaden Naira biliyan 3.5 da gwamnatin jihar Oyo da hukumominta suka amince da bankuna hudu.

Bankunan da abin ya shafa sun hada da First Bank, United Bank for Africa (UBA), Bankin Wema, da bankin Zenith.

Wannan dai na zuwa ne kwanaki bayan Gwamna Seyi Makinde ya sake lashe zaben sa karo na biyu a matsayin Gwamnan jihar.

Kudaden dai, kamar yadda kotun ta bayyana, an yi su ne domin daidaita ma’auni na Naira 3,374,889,425.60 daga shari’ar bashin da ake bin wasu tsofaffin shugabannin kananan hukumomi, da kansilolin da aka kora a ranar 29 ga Mayu, 2019, kafin karshen wa’adin su da Gwamnan Jihar Oyo,

Mai shari’a A. O. Ebong ya bayar da wannan umarni ne a lokacin da yake yanke hukunci kan karar da tsohon shugaban jam’iyyar na garnishee ya shigar da gwamna da kansiloli karkashin jagorancin Bashorun Majeed Bosun Ajuwon da Idris Okusesi.

Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a

Facebook. Alfijr Labarai
YouTube. Best Seller Channel
Twitter. @Musabestseller
Instagram. @musa_bestseller

Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijr Labarai 👇

https://chat.whatsapp.com/G1wNveF9mGU7jec5mWhFvZ

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *