Gwamnan Kano Ya Bayyana Ma’aikatun Da Aka Tura Sabbin Kwamishinonin Jihar

FB IMG 1713451480637

Gwamnan jihar Kano ya jagoranci rantsar da sabbin kwamishinoni guda hudu tare da bayyana ma’aikatan da za su fara aiki a jihar a dakin taro na Africa House dake gidan gwamnati.

Alfijir Labarai ta rawaito Gwamnan ya bayyana Mustapha Rabi’u kwankwaso a matsayin kwamishinan ma’aikatar matasa da wasanni, sai Abduljabbar Garko a matsayin kwamishinan kasa da safayo, yayin da aka tura Shehu Aliyu yarmedi a matsayin kwamishinan ayyuka na musamman sai Adamu Aliyu kibiya kwamishinan kasuwanci da masana’antu.
Gwamna Yusuf ya Kuma ja hankalinsu da su zama masu gaskiya da rikon Amana a dukkannin lamuransu na yau da kullum.

Ya kuma bukace su da su maida hankali wajen bashi damar sauke nauyin da al’ummar jihar kano suka dora masa..

Haka-zalika gwamnan ya jagoranci rantsar da sabbin masu bashi shawara da suma majalisar dokokin jihar kano ta sahalle masa ya nada su.

Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a

https://twitter.com/Musabestseller?s=09

https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165

https://www.threads.net/@alfijirlabarai

https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12

https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag

Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijir Labarai 👇

https://chat.whatsapp.com/CJ2q8cmhhOxFY6OEgwV5vk

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *