Hukumar WAEC Ta Sanar Da Fara Rubuta Jarabawar Ɗalibai Ta Kwamfuta

Shugaban hukumar na Nijeriya, Mista Patrick Areghan ne ya bayyana hakan a wata hira da manema labarai a Legas a ranar Asabar.

Alfijir Labarai ta rawaito hukumar shirya jarabawa ta yammacin Afirka (WAEC) ta sanar da wani shiri na bullo da tsarin gudanar da jarabawar kammala sakandire (WASSCE) ta kwamfuta

Shugaban hukumar na Nijeriya, Mista Patrick Areghan ne ya bayyana hakan a wata hira da manema labarai a Legas a ranar Asabar.

Areghan, wanda ya yi tsokaci kan irin nasarorin da hukumar ta samu a karkashin kulawarsa, duk da cewa, shugaban ya fara shirin mika ragamar shugabancinsa a ranar 1 ga watan Oktoba, ya bayyana cewa, bullo da tsarin gudanar da jarrabawar ta hanyar Kwamfuta (CBT) shi ne babban muradinsa a hukumar.

Areghan ya ce, baya ga bullo da shirin na CBT, yana kuma son ganin an daidaita dukkan ayyukan hukumar su zama na tsarin kwamfuta.

Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a

https://twitter.com/Musabestseller?s=09

https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165

https://www.threads.net/@alfijirlabarai

https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12

https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag

Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijir Labarai  👇

https://chat.whatsapp.com/FNim39ly65N2CzcTt8FgWb

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *