Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Kan Matar Ɗan Takarar Gwamnan Zamfara Sa’o’i 24 A Gudanar Da Zaɓe

Alfijr ta rawaito ƴan bindiga da ake zargin ‘yan daba ne sun kai hari kan matar dan takarar gwamna a jam’iyyar PDP a jihar Zamfara, Dauda Lawal Dare lamarin da aka ce ya faru a Gusau.

An ce ya hada da matar Dare, mataimakanta, da sauran masu wucewa marasa laifi.

Dare wanda ya bayyana hakan ga manema labarai a lokacin da yake ganawa da manema labarai a gidansa.

Ya bayyana cewar harin ya yi sanadin jikkata wasu mutane daban-daban.

Ya yi zargin cewa gwamnati ce ta dauki nauyin kai harin, yana mai cewa harin ya faru ne sakamakon farin jinin siyasar da jam’iyyar PDP ta samu a jihar kawo yanzu.

“Na riga na kai rahoton mummunan ci gaban da aka samu ga hukumomin tsaro a jihar, ina jiran martanin su”, in ji shi.

Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a

Facebook. Alfijr Labarai
YouTube. Best Seller Channel
Twitter. @Musabestseller
Instagram. @musa_bestseller

Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijr Labarai 👇

https://chat.whatsapp.com/KrigvNKcneVBHxctLUQ0ux

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *