Gwamnatin jihar Kano ta soke lasisin masana’antar Kannywood da gidajen Gala a fadin jihar
Alfijir Labarai ta rawaito shugaban hukumar tace fina-finai da ɗab’i ta jihar Kano, Malam Abba El-Mustapha ne ya sanar da hakan a ranar Juma’a da safe.
El-Mustapha ya ce hakan na nufin babu wanda zai ci gaba da yin fim a jihar Kano sai ya sabunta rajista da hukumar.
Wannan soke lasisin ya shafi masu fitowa a fim, da masu shiryawa, da kasuwancinsa.
Su kuma gidajen rawar Gala an dakatar da su nan take har sai an tantance su.
Aminiya
Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a
Facebook. Alfijir Labarai
YouTube. Best Seller Channel
Twitter. @Musabestseller
Instagram. @musa_bestseller
Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijir Labarai 👇
https://chat.whatsapp.com/H5oBRaZBdCVIyOTIV5eMfb