Rundunar Yan Sandan Kano Ta Damke Mamallakin Ginin Da Ya Rufta Tare Da Kashe Mutane A Unguwar Kuntau

FB IMG 1714136378072

Rundunar Yan Sandan Jihar Kano ta Bayyana Cewa ta kama Mamallakin Gini Mai Hawa Biyu Da ya rufta a Unguwar Kuntau Dake Karamar Hukumar Gwale

Alfijir Labarai ta rawaito cikin wata sanarwa da Kakakin Rundunar Yan Sandan Jihar Kano SP. Abdullahi Haruna Kiyawa ya aikewa Ammasco Radio yace, Tuni rundunar ta Fara Gudanar da bincike Kuma da zarar ta Kammala zata Gurfanar da Mamallakin Ginin gaban kotu

Rundunar Yan Sandan tace Zatayi aiki Ka fada da ka fada da Hukumar Tsara Birane ta Jihar Kano Domin Cigaba da Gudanar da bincike akan yadda aka Gaza bin Ka’idojon da suka Kamata Wajen Gudanar da Ginin

A ranar juma’a ne dai Wani Gini a Unguwar Kuntau ya rufta, Wanda Yayi Sanadiyar Mutuwar Mutane uku Yayinda wasu Mutum Biyar suka jikkata

Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a

https://twitter.com/Musabestseller?s=09

https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165

https://www.threads.net/@alfijirlabarai

https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12

https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag

Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijir Labarai 👇

https://chat.whatsapp.com/CJ2q8cmhhOxFY6OEgwV5vk

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *