Hajiya Fatima Kilishi Yari wadda a ake kira da Fatima Yusuf a lokacin da take aiki a BBC Hausa ta rasu a yau Alhamis bayan gajeriyar rashin lafiya.
Marigayiyar ta fara aiki da sashen Hausa na BBC a birnin London a shekarar 1976 sannan kuma ta yi aiki da gidan rediyon Kano a shekarun 1980.
Hajiya Fatima Kilishi ta rasu ta bar ƴaƴa da jikoki ciki har da mai taimaka wa gwamnan Kano kan hulɗa da jama’a, Hon Muhammad Jamu Yusuf.
Allah ya jikanta da rahama Ameen.
Domin samun sauran shirye shiryenmu zaku iya biyo mu ta wannan shafukan👇
https://twitter.com/Musabestseller?s=09
https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165
https://www.threads.net/@alfijirlabarai
https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12
https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag
Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijr Labarai 👇👇
https://chat.whatsapp.com/ELQRQyq1zGn7zpAVP8DwNj