Iran ta gindaya wasu sharadai 3, da za’a bi mutukar ana so ta dakatar da yaƙin da aka tsokaneta

FB IMG 1773178572804

Shugaban ƙasar Masoud Pezeshkian ya bayyana sharudda uku da Iran ta ce dole a cika kafin a kawo ƙarshen yaƙin da Amurka-Isra’ila suka kaddamar a kanta.

A wata sanarwa daya wallafa, Pezeshkian ya ce Iran na goyon bayan zaman lafiya, amma ya jaddada cewa ba za a iya kawo ƙarshen yaƙin ba sai an cika wasu muhimman sharuɗɗa.

Ya ce sharuddan sun haɗa da:

1. Amincewa da haƙƙoƙin Iran a matakin ƙasa da ƙasa.

2. Biyan diyya ga Iran kan asarar da ta yi sakamakon hare-haren da aka kai mata.

3. Samar da tabbacin ƙasa da ƙasa da zai hana sake kai mata hare-hare a nan gaba.

Shugaban ya kuma bayyana cewa Iran na da niyyar ganin an samu zaman lafiya a yankin gabas ta tsakiya, amma ya zargi Amurka da Isra’ila da haddasa rikicin da ake fama da shi a yanzu.

Ga masu son bada talla ko shawarwari a kira wannan lambar +2348032077835

Domin samun sauran shirye-shirye Alfijir labarai/Alfijir news ku biyo mu ta nan 👇

https://twitter.com/Musabestseller?s=09

https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165

https://www.threads.net/@alfijirlabarai

https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12

https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag

Alfijir labarai Alfijir News Whatsapp Group 👇👇

https://chat.whatsapp.com/H5oBRaZBdCVIyOTIV5eMfb?mode=ac_t

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *