Alfijr ta rawaito Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) ta bayyana cewa ba za ta bari masu kada kuri’a su yi amfani da wayoyinsu na hannu ba, a yayin kada kuri’unsu a ranar Asabar.
Kwamishinan zabe na jihar Ogun, Niyi Ijalaye ne ya bayyana hakan jiya a Abeokuta yayin wata tattaunawa da manema labarai, bayan ganawa da shugabannin hukumomin tsaro gabanin zaben na ranar Asabar.
Ijalaye ya ce, laifi ne ga masu kada kuri’a yin amfani da wayoyinsu na hannu a rumfunan zabe.
Ya kara jaddada cewa, wannan tsarin na daga cikin matakan da za a bi wajen hana sayen kuri’u a lokacin zabe.
Kwamishinan ya bayyana cewa ba za a bari masu kada kuri’a su amsa ko su kira waya ba, ko daukar hotuna da wayoyinsu a lokacin da suke kada kuri’a ba.
Ya kuma bayyana shirin hukumar zabe na gudanar da sahihin zabe tare da taimakon jami’an tsaro da hukumomi daban-daban da sauran masu ruwa da tsaki.
Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a
Facebook. Alfijr Labarai
YouTube. Best Seller Channel
Twitter. @Musabestseller
Instagram. @musa_bestseller
Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijr Labarai 👇