Karku Kara Bawa Gwamnatin Kano Bashi Ko Lamuni – In Ji Abba Gida Gida

Alfijr ta rawaito Zaɓaɓɓen Gwamnan Kano Engr. Abba Kabir Yusuf ya shawarci bankuna da masu bada bashi ko lamuni na gida da ƙasashen ƙetare kan su kauce wa bai wa Gwamnati mai barin gado bashi a wannan lokacin.

Abba ya zargi cewa Gwamnati mai ci ta ciyo basussuka da dama domin gadawar Gwamnati mai zuwa.

Mai magana da yawun zaɓaɓɓen Gwamnan Malam Sunusi Bature Dawakin Tofa ya yiwa freedom radio bayanin hakan.

Bature ya kara da cewa abin yana neman ya zamarwa mutanen Kano kamar muguna ne, don haka suke sake bada wannan shawara kamar yadda muka yi a baya ma.

Kin yyin hakan zai jawo rashin la akari da bashin bayan zaman su a gwamnati.

Freedom Radio

Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a

Facebook. Alfijr Labarai
YouTube. Best Seller Channel
Twitter. @Musabestseller
Instagram. @musa_bestseller

Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijr Labarai 👇

https://chat.whatsapp.com/G1wNveF9mGU7jec5mWhFvZ

2 Replies to “Karku Kara Bawa Gwamnatin Kano Bashi Ko Lamuni – In Ji Abba Gida Gida

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *