Fadar Shugaban Kasa Ta Mayar Wa Kwankwaso Martani Kan Kalaman Da Yayi Akanta

IMG 20240525 WA0104

Fadar shugaban kasa ta musanta zargin da jagoran jam’iyyar NNPP na kasa, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso ya yi na cewa gwamnatin tarayya na shirin kafa dokar ta baci a jihar Kano.

Kwankwaso ya yi zargin jam’iyyar APC a karkashin gwamnatin tarayya ta dauki bangare a rikicin Sarautar Kano.

Fadar shugaban kasar tace ba wani shiri na sanya dokar ta baci don kawar da gwamnati dimokuradiyya a wata jiha, inda ta ce “jita-jita ce kawai yake yadawa da rudani.

Mai magana da yawun shugaban kasa, Bayo Onanuga, ya shaidawa jaridar The Nation a daren Litinin cewa, babu wani yanayi da zai sa a sanya dokar ta baci a jihar.

Sai dai fadar shugaban kasar ta ce: “Babu gaskiya a ciki. Jita-jita ce kawai. Gwamnatin Tarayya ba za ta iya kafa dokar ta-baci a kowace jiha ba tare da sa hannun Majalisar Tarayya ba. Babu wannan batu wannan batu Jita-jita ce kawai.

“Majalisar dokokin kasa tana hutu. Babu wani shugaban da zai iya tashi kawai ya ayyana dokar ta-baci a kowace jiha.”

Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a

https://twitter.com/Musabestseller?s=09

https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165

https://www.threads.net/@alfijirlabarai

https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12

https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag

Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijr Labarai 👇👇

https://chat.whatsapp.com/ELQRQyq1zGn7zpAVP8DwNj

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *