Ganduje ya janye shirin kafa Hukumar Hisbah mai zaman kanta a Kano

FB IMG 1765920055949

Tsohon Gwamnan Jihar Kano, Dr. Abdullahi Umar Ganduje, ya janye shirin da ya yi na kafa wata Hisbah mai zaman kanta da ake kira Hisbah Fisabilillahi a Jihar Kano.

An bayyana wannan mataki ne cikin wata sanarwa da wani jigo a jam’iyyar APC a Kano, Dr. Baffa Babba Dan Agundi, ya fitar tare da sanya wa hannu.

A cewar sanarwar, matakin ya biyo bayan taron masu ruwa da tsaki da ya haɗa wakilai daga ƙananan hukumomi 44 na Jihar Kano. An gudanar da taron ne a Ofishin Kamfen na Tinubu.

Sanarwar ta bayyana cewa an yanke shawarar janyewa daga shirin ne bayan martanin jama’a da damuwar da aka nuna dangane da shirin kafa Hisbah mai zaman kanta.

Ga masu son bada talla ko shawarwari a kira wannan lambar +2348032077835

Domin samun sauran shirye-shirye Alfijir labarai/Alfijir news ku biyo mu ta nan 👇

https://twitter.com/Musabestseller?s=09

https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165

https://www.threads.net/@alfijirlabarai

https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12

https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag

Alfijir labarai Alfijir News Whatsapp Group 👇👇

https://chat.whatsapp.com/H5oBRaZBdCVIyOTIV5eMfb?mode=ac_t

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *