Ganganci! Jirgi Ya Jefa Wa Masu Taron Mauludin Annabi Bom A Kaduna

IMG 20231204 125258

Ana fargabar harin bom din jirgin sojin ya hallaka mutane sama da 30 a wurin taron Mauludi a kusa da filin jirgin sama na Kaduna

Alfijir labarai ta rawaito Wani jirgin soji ya jefa bom a kan masu taron Mauludi a yankin Tudun Biri da ke Karamar Hukumar Igabi a Jihar Kaduna.

Lamarin ya faru ne a misalin karfe 9 na daren Lahadi a yankin da ke kusa da Filin Jirgin Sama na Kaduna.

Wani mazaunain yankin ya ce “mutane na cikin bikin Mauludi kawai sai jirgin sama ya jefo masu bom wanda ya yayi sanadiyar mutuwar mutane sama da 30 a wurin,” inji shi.

Wasu majiyoyi sun shaida wa wakilinmu cewa akwai yiwuwar hasarar rayukan ya karu.

Kwamishinan Tsaro da Harkokin Cikin Gida na Jihar Kaduna, Samuel Aruwan ya tabbatar da faruwar lamarin, amma ya ki bayyana yawan wayanda suka rasa rayukansu ba.

Amma ya ce za su sanar da manema labarai abin da ya faru a wurin bayan sun yi taron gaggawa na majalisar tsaron jihar.

Aminiya

Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a

https://twitter.com/Musabestseller?s=09

https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165

https://www.threads.net/@alfijirlabarai

https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12

https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag

Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijr Labarai 👇👇

https://chat.whatsapp.com/H47OrRBUPHYEeNqV0vwlQp

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *