Gargaɗi! Za’a fara hukunta wadanda suke shigar da korafen karya da akan masu shari’a – In ji CJN

Mai shari'a k

Babbar Jojin kasa, Mai Shari’a Kudirat Kekere-Ekun, ta bayyana cewa bangaren shari’a na binciken hanyoyin da za a bi wajen hukunta duk wanda yayiwa wani alkali kazafi domin dakile yawan korafe korafen gaibu da ake shigarwa barkatai.

Mai shari’a Kekere-Ekun ta ce majalisar shari’a ta kasa (NJC) za ta binciki korafe-korafe na gaskiya a kan jami’an shari’a yayin da kuma za ta tallafa wa alkalan da akayiwa kazafi don tabbatar da anyi musu adalci.

Ta bayyana hakan yayin da take jawabi a wajen bude taron shekara-shekara na alkalan kotun daukaka kara a ranar Litinin a Abuja.

Mai shari’ar ta sake jaddada aniyar majalisar na sauya mumman kallon da wasu ke yiwa bangaren shari’a a tsakanin al’umma.

Ta shawarci shugabannin kotuna da su rika gudanar da tarukan bita akai-akai don kaucewa yanke hukunci masu karo da juna da kuma bin diddigin hukunce-hukuncen kotunan shari’a da dalilan yanke hukunci.

Daily Post Nigeria

Domin samun sauran shirye shiryenmu zaku iya biyo mu ta wannan shafukan👇

https://twitter.com/Musabestseller?s=09

https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165

https://www.threads.net/@alfijirlabarai

https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12

https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag

Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijr Labarai 👇👇

https://chat.whatsapp.com/ELQRQyq1zGn7zpAVP8DwNj

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *