Gwamnan Jihar Bauchi Ya bayar da Tallafin Biliyoyin Naira Ga Masu zuwa Aikin Hajjin Bana

FB IMG 1711735026880 edit 7072339794752

Gwamnan jihar Bauchi, Sen Bala Mohammed, ya amince da karin rabin kudin aikin Hajji na Shekarar 2024 ga maniyyatan jihar.

Alfijir labarai ta rawaito Hakan na nuni da cewa gwamnatin jihar ta bayar da Tallafin ₦959,000 ga kowane mahajjata 1,652 Daga jihar, wanda ya kai Naira biliyan 2.5.

Kwamishinan al’amuran addini da wayar da kan al’umma na jihar, Alhaji Yakubu Hamza ne ya bayyana hakan yayin ganawa da manema labarai a gidan gwamnati da ke Bauchi a Yau Juma’a.

Kwamishinan yace, “wadanda za su amfana da maniyyata sun hada da wadanda suka rigaya sun biya karin kudin da kuma da kuma wadanda Gwamnatin jihar ta ba su gurbin aikin Hajji.

Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a

https://twitter.com/Musabestseller?s=09

https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165

https://www.threads.net/@alfijirlabarai

https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12

https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag

Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijir Labarai 👇

https://chat.whatsapp.com/CJ2q8cmhhOxFY6OEgwV5vk

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *