Gwamnatin Kano ta ayyana ranar komawa makarantu domin fara darasi

IMG 153335 03925 1756910028093

Gwamnatin Jihar Kano ta sanar da ranar dawowar makarantu na firamare da na sakandare domin cigaba da Karatu a sabon zangon na shekarar 2025/2026.

Wata sanarwa da daraktan wayar da kai na ma’aikatar Ilimi,ta Kano Balarabe Abdullahi Kiru ya fitar ta bayyana cewa, daliban makarantu na kwana za su koma a ranar Lahadi, 7 ga Satumba, 2025, yayin da daliban makarantu na rana za su koma a Litinin, 8 ga Satumba, 2025.

An shawarci iyaye da masu kula da yara su kula da wannan jadawalin domin tabbatar da cikakken bin doka, inda aka gargadi dalibai da suka saba dokar cewa za su fuskanci hukunci.

Kwamishinan Ilimi na Jihar Kano, Dr. Ali Haruna Makoda, ya yi fatan alheri ga malamai da ɗalibai wajen sabon zangon karatu mai zuwa..

Ga masu son bada talla ko shawarwari a kira wannan lambar +2348032077835

Domin samun sauran shirye-shirye Alfijir labarai/Alfijir news ku biyo mu ta nan 👇

https://twitter.com/Musabestseller?s=09

https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165

https://www.threads.net/@alfijirlabarai

https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12

https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag

Alfijir labarai Alfijir News Whatsapp Group 👇👇

https://chat.whatsapp.com/H5oBRaZBdCVIyOTIV5eMfb?mode=ac_t

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *