Sarkin Hausawan Afirka, Sardaunan Agadas ya karramawa Dan Adaidaita da ya tsinci Miliyan 15

IMG 20231008 WA0308

Sakamakon halayyar kirki da karramawa da martaba malam Bahaushe a idon duniya, Masarautar taga dacewar karrama Auwalu mai Adaidaita daya tsinci kudi Milyan 15, tare da gidan radiyon Arewa da suka sanar da cigiyar.

A ranar asabar ne mai martaba Dr Abdulkadir Koguna sarkin Hausawan Afirka kuma Sardaunan Agadas ya bawa Auwalu salisu Ambasadan Hausawan Afirka.

Baya ga haka masarautar ta naɗa shi Ɗan Amanar Hausawan Afirika, wanda a karshen shekarar nan za a yi bikin nadin

Haka kuma masautar ta karrama Arewa Radio bisa wannan kokarin da suka yi suma.

Mai Martaba ya kara kira matasa da suyi riko da gaskiya da amana a dukkan lamuransu, kuma suyi koyi da Auwalu, domin ya nuna akwai na Allah a cikin masu sana’arsu ta adaidaita Sahu.

IMG 20231008 WA0298
IMG 20231008 WA0301
IMG 20231008 WA0312

Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a

https://twitter.com/Musabestseller?s=09

https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165

https://www.threads.net/@alfijirlabarai

https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12

https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag

Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijir Labarai 👇

https://chat.whatsapp.com/K8z1chFesJeCf99QehWJPo

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *