Kasar Iran ta naɗa Ayatullah Arafi a matsayin Jagoran Ƙoli na wucin gadi bayan rahoton mutuwar Ali Khamenei a wani hari ta sama da Amurka da Isra’ila suka kai a ranar Asabar.
An sanar da wannan naɗin ne yayin da ƙasar ta fara shirye-shiryen sauyin jagoranci a hukumance.
Ayatullah Arafi zai riƙa gudanar da ayyukan Jagoran Ƙoli har sai Majalisar Ƙwararru (Assembly of Experts), wadda kundin tsarin mulki ya ɗora wa alhakin naɗawa da sa ido kan mafi girman muƙamin ƙasar, ta zaɓi magaji na dindindin.
Daidai da tanade-tanaden dokokin Iran kan gadon mulki, Arafi zai yi aiki a cikin kwamitin wucin gadi na mambobi uku tare da Shugaba Masoud Pezeshkian da Babban Alkalin Ƙasa Gholamhossein Mohseni-Ejei. An ba kwamitin alhakin kula da ayyukan Jagoran Ƙoli a lokacin miƙa mulki.
Arafi mai shekaru 67, babban malamin addini ne wanda ya shafe shekaru da dama yana aiki a harkokin addini da siyasa a Iran.
Ya taɓa zama mamba a Majalisar Masu Tsaron Kundin Tsarin Mulki (Guardian Council), kuma Majalisar Tantance Maslahar Ƙasa (Expediency Discernment Council) ta tabbatar da shi a matsayin mamba a kwamitin wucin gadi.
Ya yi karatu a birnin Qom, cibiyar manyan makarantu na addini mafi girma a Iran, ƙarƙashin fitattun malamai, inda ya kai matakin mujtahidi, wanda ke ba shi ikon fitar da hukunce-hukuncen shari’a na Musulunci da kansa.
Ga masu son bada talla ko shawarwari a kira wannan lambar +2348032077835
Domin samun sauran shirye-shirye Alfijir labarai/Alfijir news ku biyo mu ta nan 👇
https://twitter.com/Musabestseller?s=09
https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165
https://www.threads.net/@alfijirlabarai
https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12
https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag
Alfijir labarai Alfijir News Whatsapp Group 👇👇
https://chat.whatsapp.com/H5oBRaZBdCVIyOTIV5eMfb?mode=ac_t