Kotu ta daure wasu mutane 2 bisa laifin damfarar Alh Aminu Dantata da ATM Gwarzo

FB IMG 1708020196814

Kotun majistare mai zamanta a Gyadi-Gyadi, Kano ta yanke wa Bukar Galadima da Suleiman Ahmed hukuncin daurin gidan yari bayan samun su da laifin zamba kan attajirin nan na Kano, Alhaji Aminu Dantata da kuma tsohon karamin ministan gidaje da ci gaban birane, Abdullahi Tijjani Gwarzo.

Alfijir labarai ta rawaito ma zambatan sun yi hadin baki domin damfarar Dantata Naira miliyan 5, da Gwarzo Naira miliyan 1.

Galadima ya yi ikirarin cewa shi ne tsohon Ministan Babban Birnin Tarayya, Injiniya Abba Gama, inda ya nemi taimakon kudi na magani daga wurin Dantata, wanda ya aika masa da naira miliyan biyar, sai daga baya aka gano cewa Gama bai nemi wannan bukata ba.

Dantata ya kai rahoton ga Hukumar Koke da Yaki da Cin Hanci da Rashawa ta Jihar Kano, inda aka kama Galadima da Ahmed aka gurfanar da su a gaban Mai Shari’a Umma Sani Kurawa, wadda ta same su da laifin hada baki wajen aikata zamba.

Kurawa ta yanke musu hukuncin daurin watanni shida ko biyan tarar naira dubu 30  da kuma watanni uku saboda kage ko tarar naira dubu 20, sai kuma wata shida ko tarar naira dubu 20 saboda cin amana.

Kano: Kotu ta daure wasu mutane 2 bisa laifin damfarar Dantata da ATM Gwarzo

Kotun majistare mai zamanta a Gyadi-Gyadi, Kano ta yanke wa Bukar Galadima da Suleiman Ahmed hukuncin daurin gidan yari bayan samun su da laifin zamba kan attajirin nan na Kano, Alhaji Aminu Dantata da kuma tsohon karamin ministan gidaje da ci gaban birane, Abdullahi Tijjani Gwarzo.

Masu laifin sun yi hadin baki domin damfarar Dantata Naira miliyan 5, da Gwarzo Naira miliyan 1.

Galadima ya yi ikirarin cewa shi ne tsohon Ministan Babban Birnin Tarayya, Injiniya Abba Gama, inda ya nemi taimakon kudi na magani daga wurin Dantata, wanda ya aika masa da naira miliyan biyar, sai daga baya aka gano cewa Gama bai nemi wannan bukata ba.

Dantata ya kai rahoton ga Hukumar Koke da Yaki da Cin Hanci da Rashawa ta Jihar Kano, inda aka kama Galadima da Ahmed aka gurfanar da su a gaban Mai Shari’a Umma Sani Kurawa, wadda ta same su da laifin hada baki wajen aikata zamba.

Kurawa ta yanke musu hukuncin daurin watanni shida ko biyan tarar naira dubu 30  da kuma watanni uku saboda kage ko tarar naira dubu 20, sai kuma wata shida ko tarar naira dubu 20 saboda cin amana.

Domin samun sauran shirye shiryenmu zaku iya biyo mu ta wannan shafukan👇

https://twitter.com/Musabestseller?s=09

https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165

https://www.threads.net/@alfijirlabarai

https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12

https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag

Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijr Labarai 👇👇

https://chat.whatsapp.com/ELQRQyq1zGn7zpAVP8DwNj

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *