Kotun Ɗaukaka Ƙara Ta Kwace Kurejar Ɗan Majalisar Wakilai Sakamakon Takaitattun Karatun Bogi

Shari'ar Zabe

Kotun daukaka kara ta tabbatar da korar Aminu Chindo, ta tare da umurta INEC ta ba Sani Dallami na jam’iyyar APC shedar lashe zaben dan majalisar wakilai ta mazabar birnin Katsina

Alfijir Labarai ta rawaito Kotun dake zamanta a Abuja ranar Laraba, ta tabbatar da hukuncin kotun korafe-korafen zabe dake Katsina, wadda ta kori dan majalisar wakilai na mazabar cikin birnin Katsina Hon Aminu Chindo na jam’iyyar PDP.

A zaman kotun na kotun daukaka kara, wadda ita ce kotun karshe dake sauraron kararrakin zaben yan majalisun dokoki, ta umurci hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa INEC ta ba Hon Sani Dallami satifiket din lashe zabe, ta kuma umurci wanda ake karar da ya bayar da tarar Naira miliyan ɗaya ga Sani Dallami bisa bata masa lokaci da ya yi

Kotun ta ƙwace kujerar Hon. Aminu Chindo ne, sakamakon laifin amfani da takardun bogi wanda kotu ta same shi dasu, wajen shigar da bayanan takara.

📸 Katsina Post
📸 Katsina Post

Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a

https://twitter.com/Musabestseller?s=09

https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165

https://www.threads.net/@alfijirlabarai

https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12

https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag

Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijir Labarai 👇

https://chat.whatsapp.com/KpTjEvHUjd3CVzIQp8CSkZ

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *