Labari Mai Dadi! Gwamnan Katsina Ya Amince Da Baiwa Ma’aikatan Jihar N 45,000 Goron Sallah

FB IMG 1702067553881

Gwamnan jihar Katsina, Mallam Dikko Umaru Radda ya amince da bai wa ma’aikatar jihar goron sallah a naira 15,000.

Alfijir labarai ta rawaito cikin wata sanarwa da gwamnan ya wallafa a shafinsa na X, ya ce sakamakon yanayin matsin rayuwa da ake ciki, ya amince da bayar da naira 45,000 ga ma’aikatan jihar da na ƙananan hukumomi.

”Sai dai naira 30,000 daga cikin kuɗin zai kasance bashi ne gwamnati ta ba su, wanda kuma za su biya cikin wata uku masu zuwa, inda za a riƙa cire naira 10,000 a cikin albashinsu a kowane wata daga Yuli zuwa Satumba”, in ji sanarwar.

Gwamna Dikko Radda ya ce ya yi hakan ne domin bai wa ma’aikatan jihar da ya kira ”haziƙan ma’aikata” su samu damar gudanar da shagulgulan bukukuwan babbar sallah cikin walwala, duba da halin matsin rayuwa da ake ciki.

Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a

https://twitter.com/Musabestseller?s=09

https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165

https://www.threads.net/@alfijirlabarai

https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12

https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag

Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijr Labarai 👇👇

https://chat.whatsapp.com/ELQRQyq1zGn7zpAVP8DwNj

Slide Up
x

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *