Majalisar Shari’ar Musulunci Ta Naɗa Dr Bashir Aliyu Umar Sabon Shugabanta

FB IMG 1746032563080

Majalisar Shari’ar Musulunci ta Najeriya (NSCJ) ta sanar da naɗin Sheikh Dr. Bashir Aliyu Umar a matsayin sabon shugaban majalisar, biyo bayan rasuwar tsohon shugaban majalisar, Sheikh AbdulRasheed Hadiyyatullah.

Sanarwar da sakataren majalisar, Malam Nafiu Baba Ahmed, ya fitar a yau Laraba, ta bayyana cewa Sheikh Bashir, wanda ke rike da mukamin mataimakin shugaba a baya, ya hau kujerar shugabanci kai tsaye bisa tsarin da ke akwai.

Sheikh AbdulRasheed Hadiyyatullah ya rasu ne a ranar Litinin da ta gabata yana da shekara 81 a jihar Osun, inda ya kwashe shekaru da dama yana jagorantar harkokin majalisar da kuma ba da gudummawa wajen ci gaban shari’ar Musulunci a Najeriya.

Majalisar ta kara da cewa za a sanar da sabon mataimakin shugaban majalisar a wani lokaci mai zuwa.

Sheikh Dr. Bashir Aliyu Umar, wanda aka nada shugaban majalisar, sanannen malami ne a fagen ilimin addini da kuma limamin masallacin Juma’a na Al-Furqan da ke jihar Kano. Ya shahara da ilimi mai zurfi da kuma kishin addinin Musulunci.

Domin samun sauran shirye-shiryen Alfijir labarai/Alfijir news ku shiga nan  👇

https://twitter.com/Musabestseller?s=09

https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165

https://www.threads.net/@alfijirlabarai

https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12

https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag

Alfijir labarai Alfijir News Whatsapp Group 👇👇

https://chat.whatsapp.com/KoLt2IMlnQfJPP6zNrcNKD

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *