NEMA Ta Yi Gargaɗin Samun Ambaliya A Jihar Kano Da Wasu Jihohi 13

Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA) ta ce jihohi 14, za su iya fuskantar ruwan sama kamar da bakin kwarya wanda zai iya haifar da ambaliya daga ranar 4 zuwa 8 ga watan Yuli a duk faɗin ƙasar.

Alfijir Labarai ta rawaito hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun Mista Ibrahim Farinloye, Kodinetan yankin, NEMA, ofishin yankin Legas ya sawa hannu.

Farinloye ya bukaci masu ruwa da tsaki a jihohin da abin ya shafa da su dauki matakan kariya domin dakile asarar rayuka da dukiyoyi.

Ya lissafa jihohi da al’ummomi a matsayin Plateau: Langtang da Shendam;

Jihar Kano: Sumaila, Tudun wada;

Jihar Sokoto: Shagari, Goronyo da Silame;

Delta: Okwa.

Sauran sun hada da jihar Kaduna: Kachia;

Akwa Ibom: Upenekang;

Adamawa: Mubi, Demsa, Song, Mayo-Belwa, Jimeta, da Yola;

Jihar Katsina: Katsina, Jibia, Kaita da Bindawa.

Ya kuma kara da jihar Kebbi: Wara, Yelwa da Gwandu;

Zamfara: Shinkafi da Gummi

Borno: Briyel;

Jigawa: Gwaram;

Kwara: Jebba;

Nijar: Mashegu da Kontagora

Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a

Facebook. Alfijir Labarai
YouTube. Best Seller Channel
Twitter. @Musabestseller
Instagram. @musa_bestseller

Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijir Labarai 👇

https://chat.whatsapp.com/GdLiqZyHuSz5NhjdGoGRGZ

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *