Shawara: Masu Gine-Gine A Filayen Gwamnatin Kano Su Dakata-Abba


Alfijr ta rawaito Zababben Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf ya shawarci ɗaiɗaikun mutane da kungiyoyi masu gine-gine a filayen gwamnatin jihar da su dakata nan take.

Sanarwar na kunshe ne cikin wani sako da ya wallafa safiyar Juma’a a shafinsa na Facebook.

A cewarsa, “kamar yadda muka kudiri aniyar dawo da tsarin birnin Kano, ina shawartar jama’a da su daina duk wani aikin gine-gine a filayen gwamnati, a ciki da wajen makarantu.

“Wuraren addini da na al’adu, da dukkan asibitoci, da makarbarta, da kume gefen katangar birnin Jihar Kano ganuwa. ”

Haka kuma, a kunshin sanarwar da mai magana da yawun zababben gwamnan, Sanusi Bature Dawakin-Tofa ya fitar, an kuma shawarci dakatar da rushewa ko kuma ci gaba da aikin duk wasu gine-gine a filayen gwamnatin jihar.

 
Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a

Facebook.   Alfijr Labarai
YouTube.     Best Seller Channel
Twitter.        @Musabestseller
Instagram.  @musa_bestseller

Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijr Labarai 👇

https://chat.whatsapp.com/G1wNveF9mGU7jec5mWhFvZ

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *