Tsadar Rayuwa! Kungiyar NLC Ta Dage Zanga-zangar Ranar Laraba

FB IMG 1709030149536

Kungiyar Kwadago ta Najeriya, NLC ta sanar da janye zanga-zangar neman saukin tsadar rayuwa a ranar ta biyu wato ranar Laraba.

Alfijir labarai ta rawaito Kungiyar ta ce ta dage zanga-zangar ne ta ranar Laraba ne saboda ta sake bai wa gwamnati karin makonni biyu har zuwa 13 ga watan Maris domin biyan bukatunta.

A ranar Talata ranar farko ta zanga-zangar, daruruwan masu zanga-zangar neman saukin matsin rayuwa da ake ciki a Najeriya ne suka fantsama kan titunan biranen kasar bisa umarnin kungiyar ta kwadago.

Kungiyar kwadago dai ta yi kira da a yi zanga-zangar gargadi ta kwana biyu. To sai dai yanzu kungiyar ta sanar da janye zanga-zangar ta rana ta biyu wato ranar Laraba 28 ga watan Fabrairu.

Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a

https://twitter.com/Musabestseller?s=09

https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165

https://www.threads.net/@alfijirlabarai

https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12

https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag

Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijr Labarai 👇👇

https://chat.whatsapp.com/H3iC9eVfJI012LJzvCQn5V

Slide Up
x

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *