Kotun majistre mai lamba 26 ta aike da wani magidanci Adamu Ibrahim gidan yari bisa zarginsa da hallaka matarsa ta hanyar buga mata dutsen guga a fuska.
Alfijir Labarai ta ruwaito lamarin ya faru ne a garin Kwanar Dangora da ke karamar hukumar Kiru a Jihar Kano.
Adamu ya bayyana cewar sabani ne ya shiga tsakaninsa da matarsa dalilin wata mata da ta nuna ba ta son mu’amalarsa da ita.
Sai dai ya ce ya yi ƙoƙarin fahimtar da ita, amma abin ya ci tura, inda ta ce babu ita babu zama da kishiya.
Daga nan ne a cewarsa ta kama shi da kokawa, kuma duk da ihun da yake yi ta ki rabuwa da shi, har ya aikata abinda ya aikata
Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a
https://twitter.com/Musabestseller?s=09
https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165
https://www.threads.net/@alfijirlabarai
https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12
https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag
Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijir Labarai 👇
https://chat.whatsapp.com/CJ2q8cmhhOxFY6OEgwV5vk