Wani Magidanci Ya Ragargaje Ƴan Bindiga Lokacin Da Suka Kai Masa Hari

A daren jiya Asabar ne ƴan bindiga suka kai hari Gidan Wakilin Nufawan Tafa Alh Mohammed Makusidi dake Garin Sabon Wuse a Karamar Hukumar Tafa ta Jihar Neja inda suka ringa yiwa gidan ruwan harsashai.

Alfijir Labarai ta rawaito wani makwafcin Sarkin Nufawan ya bayyanawa wakilin mu cewa, a yayin da Magidanci ya buɗe kofa ne ya shammace su ya halbi daya daga cikin ƴan bindigan wanda nan take ya fadi, Sannan ya samu daya a kafa wanda daga baya aka gano wani makwafcin sa ne dake kiwon shanu kusa da gidan sa.

A makon daya gabata a ranar Asabar ƴan bindiga sun kai hari gidan shugaban karamar hukumar ta Tafa in da nan ma basu sha da dadi ba.

Har izuwa yanzun dai babu wata sanarwar daga hukumomin tsaro ko bangaren Gwamnati dangane da harin.

Tsalle Daya

Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a

https://twitter.com/Musabestseller?s=09

https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165

https://www.threads.net/@alfijirlabarai

https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12

https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag

Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijir Labarai 👇

https://chat.whatsapp.com/FNim39ly65N2CzcTt8FgWb

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *