Shugaban NLC na ƙasa, Kwamared Joe Ajaero ne ya sanar da hakan a wani taron manema labarai da ya gudana a Babban Ofishin NLC na Ƙasa da ke Abuja
Alfijir labarai ta ruwaito Ƙungiyar Ƙwadago ta Nijeriya NLC ta tsunduma yajin aikin sai baba ta gani bayan rashin cimma matsaya da Gwamnatin Tarayya kan mafi ƙarancin albashin ma’aikata.
’Yan ƙwadagon a wannan Juma’ar sun sanar da shiga yajin aikin kai tsaye kan abin da suka kira hawa kujerar naƙi da Gwamnatin Tarayya ta yi na sauya matsayarta kan mafi ƙarancin albashi ma’aikata.
Wannan na zuwa ne a yayin da NLC ta yi fatali da tayin N60,000 a matsayin mafi ƙarancin albashin ma’aikata da Gwamnatin Tarayyar ta gabatar.
Shugaban NLC na ƙasa, Kwamared Joe Ajaero ne ya sanar da hakan a wani taron manema labarai da ya gudana a Babban Ofishin NLC na Ƙasa da ke Abuja.
Kwamared Ajaero ya ce yajin aikin zai fara ne kai tsaye daga ƙarfe 12:00 na daren Lahadi wayewar gari Litinin.
Aminiya
Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a
https://twitter.com/Musabestseller?s=09
https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165
https://www.threads.net/@alfijirlabarai
https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12
https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag
Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijr Labarai 👇👇
https://chat.whatsapp.com/ELQRQyq1zGn7zpAVP8DwNjJami’an tsaro a Jamhuriyar Nijar sun yi nasarar cafke ƙasurgumin ɗan bindigar nan Ɓaleri, wanda ake nema ruwa a jallo a Najeriya.
Dakyau