Nijar Ta Tsawaita Dokar Ta Baci A Wasu Jihohi A Kasar

Alfijr ta rawaito Gwamnatin Jamhuriyar Nijar ta sanar da tsawaita dokar ta- bacin da ta sanya a wasu jihohin kasar da suke fama da matsalar hare-haren kungiyoyin masu tayar da kayar ba.

Ta bayyana haka ne bayan taron majalisar ministocin kasar da aka gudanar a ranar Alhamis wanda Shugaba Mohamed Bazoum ya jagoranta.

Jihohin da lamarin ya shafa su ne Diffa, Tawa da Tillaberi.

Dokar za ta fara aiki daga ranar 1 ga watan Mayu zuwa ranar 29 ga watan Yuli na 2023.

Gwamnati za ta mika bukatar tsawaita dokar ta-bacin ga majalisar dokoki don neman amincewar ta.

Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a

Facebook. Alfijr Labarai
YouTube. Best Seller Channel
Twitter. @Musabestseller
Instagram. @musa_bestseller

Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijr Labarai 👇

https://chat.whatsapp.com/G1wNveF9mGU7jec5mWhFvZ

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *