Irin Illolin Da Takunkumin ECOWAS Ya Fi Yiwa Al’ummar Najeriya Musamman Masu Iyaka Da Nijar

Muna rokon gwamnati da ta gaggauta samar wa ‘yan Najeriya sauki akan matsanancin tsadar abinci da ake fama dashi a kasa

Alfijir Labarai ta rawaito Shugaban Babbar Kasuwar Maigatari a Jihar Jigawa, Muhammadu Ibrahim ya bayyana damuwarsa kan cewar bai taɓa tunani ko sau ɗaya za a iya samun dambarwar diflomasiyya tsakanin Najeriya da Nijar ba.

Hakan na kunshe ne cikin wata tattaunawa da yayi da Premium Times.

Ya kara da cewa wannan dambarwa wadda ta janyo rufe kan iyakar Najeriya da Nijar, ta janyo dubban masu zuwa cin kasuwar Maigatari daga Nijar da Najeriya cikin gagarumin matsanancin ƙuncin rayuwa.

Da ya ke bayanin irin mawuyacin halin da jama’a su ka shiga saboda daina hada-hada a kasuwar da ke kusa da kan iyakar Najeriya da Nijar, Ibrahim ya ce takunkumin da aka ƙaƙaba wa Nijar ya durƙusar da harkokin kasuwanci a kasuwar Maigatari.

“Irin gagarumin kasuwancin da ke gudana tsakanin Najeriya da Nijar abu ne da ba za a iya ƙididdigewa ba.

“Ban taɓa tunani cewa wai Najeriya da Nijar za a yi yaƙi ba, saboda irin kusancin dangantakar da ke a tsakanin mu.

Saboda dukkan mu dai ɗaya mu ke. ‘ya’yan mu da matan mu wasu duk a Nijar su ke da zama, su ma na su na nan zaune a Najeriya.

“Mu dai na mu shi ne yin kira da roƙo ga Shugaba Bola Tinubu ya yi tunanin sasanta rikicin nan cikin ruwan sanyi, domin harkokin kasuwanci ya dawo kamar yadda ya ke a baya.”

Kasuwar Maigatari kasuwa ce mai ci a kowane mako, wadda akasari ta yi suna da tarihi wajen hada-hadar shanu.

Dubban mutane daga Najeriya, Nijar, Afrika ta Tsakiya, Mali da wasu ƙasashen Afrika ta Tsakiya duk su na cin kasuwar.

Lokacin da wakilin mu ya ke kasuwar, fayau ya same ta, ba kowa.

Haka ita ma kan iyakar Najeriya da Nijar da ke Maigatari a kulle ta ke.

A nasa bangaren wani dillalin shanu a Kasuwar Maigatari, mai suna Muhammadu Ɗanduwa, wanda ya yi magana a madadin sauran dillalan shanu, ya bayyana irin dimbin asarar da ake yi sakamakon hana tsallakowa daga Nijar zuwa Maigatari.

Ya ce mazauna yankin na tsakiyar zaman raɗaɗin tsadar rayuwar da su ka afka bayan cire tallafin fetur, sai kuma su ka fuskanci gurguncewar harkokin kasuwanci, sanadiyyar saka wa Nijar takunkumi da kulle kan iyakokin Nijar ɗin.

“Dubi dai kasuwar nan, ba don takunkumi ba da ba za ka zo a yau washegarin cin kasuwar ba ma har ka samu wurin da za ka ajiye mota. Saboda cinkoson mutane masu zuwa hada-hadar cinikin shanu.

“Kafin takunkumin, kamar yanzu ba zan iya ƙirga yawan shanun da na yi wa dillanci ba, amma dubi yau ko mutum ɗaya ba wanda ya yi mani magana.

“Baya ga cinikin shanu, da yawa masu zuwa yi mana aikin noma daga cikin Nijar su ke tsallakowa, to a yau sun daina, ga amfanin gonar mu can tsaye, duk ciyawa ta cika gonakin mu.” Inji Ɗanduwa.

Jigawa na ɗaya daga cikin jihohin Najeriya bakwai da suka kan iyaka da Nijar.

Sauran jihohin sun haɗa da Barno, Yobe, Katsina, Zamfara, Sokoto da Kebbi.

Kakakin Yaɗa Labaran Shugaba Tinubu, Abdul’aziz Abdul’aziz ya ce Tinubu na yin taka-tsantsan da irin kyakkyawar dangantakar da ke tsakanin Najeriya da Nijar.

Ya ce akwai farfaganda da wasu ke yaɗuwa kan kai wa Nijar hari.

“Amma gaskiyar magana, ana ta ƙoƙarin sulhuntawa ta hanyar diflomasiyya.” Inji shi.

Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a

Facebook. Alfijir Labarai
YouTube. Best Seller Channel
Twitter. @Musabestseller
Instagram. @musa_bestseller

Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijir Labarai 👇

https://chat.whatsapp.com/Jmw5CBsPV6H3DbSgnlFUHM

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *