Aisha Buhari bata da ikon ba wa ma’aikatan FG izinin ba hutu-Inji Wasu Manyan Lauyoyi

Aisha Buhari bata da ikon ba wa ma’aikatan FG izinin ba hutu

Best Seller Channel 

Best Seller Channel 
Wasu Manyan Lauyoyin Najeriya guda uku sun martani ga  umarnin Mai dakin shugaban kasa, Muhammadu Buhari  na cewa ma’aikatan da ke ofishinta su tafi hutun da ba a iya gani ba.
 Sun ce Aisha Buhari Umarnin nata ya zo ta  ba bisa ka’ida ba domin ba ta da hurumin bayar da irin wannan umarni, sai shugaban ma’aikatan gwamnatin tarayya, ce kawai ke da ikon haka. 
jaridar PUNCH ranar Asabar ta rawaito 
manyan lauyoyin uku, da suka hadar da Ebun-Olu Adegboruwa, Lekan Ojo da Ifedayo Adedipe, sun bayyana haka ne a wata tattaunawa daban-daban da suka yi  da ita. 
Sun sake bayyana cewar wadanda ke aiki tare da shugaban kasa da matarsa ​​suna yiwa al’ummar Najeriya aiki kuma ana biyansu da kudaden kasa.
 A yayin da ake ta rade-radin samun juna biyu, babban mai ba shugaban kasa shawara kan harkokin lafiya a ofishin uwargidan shugaban kasa, Mohammed Kamal, a ranar 21 ga Disamba, 2021, ya sanar da cewa Aisha ta umurci dukkan ma’aikatan ofishinta da su ci gaba da tafiya hutun Sai Baba ta gani.
Best Seller Channel 

Zancen ko matar shugaban kasa na da juna biyu ko kuma tana da wani ciwo ba shi da alaka da daukar ma’aikatan gidanta aiki a karkashin doka. 
Ya Kara da cewa, na yi imanin fadar shugaban kasa, za ta duba hakan, domin kada uwargidan shugaban kasa ta dauki doka a hannunta, domin abin da ta yi ya wuce gona da iri. 
 Ya sake bayyana cewa, ya kamata shugaban ma’aikatan ya gaggauta kiran wadannan ma’aikatan, domin hakan na iya zama mummunan misali ga hatta matan gwamnoni ko matan aure da sauran jami’ai, wadanda za su rika daukar ma’aikatan gwamnati tamkar ma’aikatansu ne ba gidajensu. 
Best Seller Channel 
 A nasa bangaren, Ojo ya ce tun farko kundin tsarin mulkin kasar bai amince da ofishin uwargidan shugaban kasar ba. 
Ya sake bayyana cewa, “Babu shakka ofishin matar shugaban kasa, kundin Tsarin Mulki bai san shi ba. 

Slide Up
x