BIRTANIYA Ta Hana Yan Nageria Shiga Kasarta

Birtaniya Ta Hana Matafiya Daga Najeriya Shiga Kasarta

Best Seller Channel 

Best Seller Channel 

Kasar Birtaniya ta haramta wa matafiya daga Najeriya shiga kasarta saboda bullar kwayar cutar COVID-19 samfurin Omicron.

Jaridar Aminiya ta rawaito Hukumomin kasar sun sanya sunan Najeriya a cikin jerin kasashen da ta hana bakinsu shiga kasarta ne a ranar Asabar.

Best Seller Channel 

Wata sanarwar da Gwamnatin Birtaniya ta fitar ta ce, “Za a sanya Najeriya a cikin jerin kasashen daga karfe 4 na asuba ranar Litinin 6 ga Disamba saboda bullar kwayar cutar Omciron da aka samu a kasar da kuma mutum 134 da suka harbu da ita a fadin kasar Birtaniya.

A makon nan ne da dai Hukumar Yaki da Cututttuka Masu Yaduwa (NCDC) ta tabbatar da harbuwar mutum uku da kwayar cutar Omicron a Najeriya.

Umarnin bai shafi matafiya ’yan kasar Birtaniya da mazauna da ’yan kasar Irelanda ne kadai za a bari su shigo kasar daga Najeriya.

Best Seller Channel 

Su ma din, “Wajibi ne a killace su na tsawon kwana 10 a cibiyoyin da gwamnati ta tanadar inda za a yi musu gwajin PCR sau biyu, a matsayi matakin dakile kwayar cutar.”

Sai dai ta ce matakin da ta dauka na wucin gadi ne a halin yanzu

Best Seller Channel 

Slide Up
x