Cushe! ‘Yan Majalisar Wakilai A Najeriya Sun Gayyaci Ministan Lafiya Bisa Zargin Karkatar Da Dala Miliyan 300

FB IMG 1710882676943

Kwamitin Majalisar wakilai mai yaki da cutar zazzabin cizon sauro, HIV/AIDS, da tarin fuka, Ya gayyaci Mohammed Pate, ministan lafiya da walwalar jamaā€™a, kan zargin karkatar da dala miliyan 300 na kuɗaɗen yaki da zazzabin cizon sauro.

Alfijir labarai ta rawaito shugaban kwamitin,Amobi Ogah ne ya sanar da hakan a wani zama da suka yi a Abuja A Yau Talata.

Ogah ya nuna rashin jin dadinsa da rashin halartar babban sakatariyar maā€™aikatar a taron kwamitin, inda yace idan har ta gaza bayyana bayan sammaci uku, za a kama ta.

“Maleriya ta zama annoba a Najeriya, duk da cewa Gwamnati ta ware kudade tun daga Shekarar 2021. Sai dai a mafi yawan lokuta ma’aikatan Gwamnati na haifar da kalubale,” inji Amobi Ogah.

Ya jaddada cewa wannan ita ce gayyata ta uku da aka yi wa sakatare na dindindin domin fayyace yadda ake amfani da kudaden. Kwamitin na neman amsoshi kan ko an yi amfani da kuɗaɗen da kuma inda suke a halin yanzu.

ā€œShin sun yi amfani da kudin? Idan ba su yi amfani da kuɗin ba, ina kuɗin? Magana ce mai sauʙi. Amma sun yi ta gudu suna kiran mutane iri-iri domin su yi magana da mu,ā€ inji shi.

Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a

https://twitter.com/Musabestseller?s=09

https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165

https://www.threads.net/@alfijirlabarai

https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12

https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag

Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijir Labarai šŸ‘‡

Majalisa https://chat.whatsapp.com/CJ2q8cmhhOxFY6OEgwV5vk

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *