A Ikeja, babban birnin jihar Legas, wani jirgi mai saukar ungulu da har yanzu ba a tantance shi ya fada kan wani gini.
Jirgin ya kone kurmus a kusa da filin jirgin saman Murtala Muhammed (MMIA), inda ya nufa.
Ko da yake an kubutar da mutane biyu da ake kyautata zaton matukin jirgin helikwaftan ne, ba a san adadin fasinjojin da ke cikin jirgin ba.
Jami’an bayar da agajin gaggawa na Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Kasa (NEMA) suna nan a wajen suna bada tallafin gaggawa.
Karin bayani na nan tafe…
Daily Trust
Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a
Facebook. Alfijir Labarai
YouTube. Best Seller Channel
Twitter. @Musabestseller
Instagram. @musa_bestseller
Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijir Labarai 👇
https://chat.whatsapp.com/H5oBRaZBdCVIyOTIV5eMfb