Yau aka tura sunayen mutane 28 da za a nada a matsayin ministocin kamar yadda kundin tsarin mulkin tarayyar Najeriya na 1999 ya bukata.
Alfijir Labarai ta rawaito Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio, ya karanta jerin sunayen mutane 28 a gaban Majalisar a yau Alhamis.
Bayan da Shugaban Majalisar ya karanto sunayen wadanda za’a nada din, sai dai da alama har yanzu akwai sunayen da ba fada ba, lamarin da ke nuni da cewa Shugaba Tinubu zai sake tura karin sunayen wasu nan gaba.
Sai dai a jihar Kano Gidajen siyasar biyu wato NNPP karkashin jagorancin Rabi’u Musa Kwankwaso da kuma jam’iyyar APC karkashin jagorancin Abdullahi Umar Ganduje, sun shiga rudani na rashin Jin sunan wani daga Kano.
Bincike ya bayyana dalilin da yasa ba’a saka sunan kowanne mutum daga kano ba, shi ne yadda ‘yan jam’iyyar APC karkashin Ganduje ke matsawa shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu lamba kan kada ya nada Kwankwaso a majalisar ministoci karkashin gwamnatin APC.
Majiyar ta bayyana cewa sansanin Gandujiyya sun dage cewa sun gwammace su rasa kujerar minista da a baiwa babban abokin hamayyarsu, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso kujerar minista, wanda ya jagoranci faduwar jam’iyyarsu a zaben 2023 a Kano.
Nigerian Tracker
Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a
Facebook. Alfijir Labarai
YouTube. Best Seller Channel
Twitter. @Musabestseller
Instagram. @musa_bestseller
Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijir Labarai 👇
Allah ya kara kare mana kasarmu, allahumma ameen
Allah ya kyauta
Wannan ba gaskiya ba ne.