Alfijr ta rawaito Hukumar tsaro ta DSS ta bayar da wa’adin sa’o’i 48 ga Kamfanin Man Fetur na Najeriya NNPC da ‘yan kasuwar man fetur da su samar da man fetur a fadin kasar nan.
Kakakin Hukumar, Peter Afunanya, ne ya bayar da wannan umarni a lokacin da yake zantawa da manema labarai a ofishinta da ke Abuja a ranar Alhamis, bayan wata ganawar sirri da suka yi da masu ruwa da tsaki a harkar man fetur.
Afunanya ya bayyana cewa kamfanin na NNPC ya tabbatar a yayin taron cewa yana da isassun kayayyakin da za su yi wa ‘yan Najeriya hidima a kowane lokacin.
. Ya ce an sanya dukkan umarnin DSS a kan jajircewa kuma za su fara aiki domin gurfanar da wadanda suka saba doka.
Afunanya ya kuma koka da kalubalen karancin man fetur, inda ya ce an dauki matakin da ke da illa ga tsaron kasar.
Domin Samun sauran shirye shiryenmu a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijr Labarai