Alfijr ta rawaito EFCC ta ce ta gurfanar da wasu makusantan gwamnan jihar Kogi a gaban kotu, ciki har da matarsa, Rashida Bello.
Hukumar tana zargin su ne da laifukan da suka shafi ɓarnata dukiya da halasta kuɗin haram na sama da naira biliyan uku.
A nata bangaren babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ƙarƙashin Mai shari’ah Obiora Egwuatu ta aike da tsare ɗan’uwan gwamnan mai suna Ali Bello a gidan gyaran hali da tarbiyya.
EFCC ta gurfanar da Abba A Dauda da Yakubu Siyaka, Adabenege da Iyada Sadat sai kuma Rashida Bello wadda EFCC ta ce tana neman ta ruwa a jallo.
Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a
Facebook. Alfijr Labarai
YouTube. Best Seller Channel
Twitter. @Musabestseller
Instagram. @musa_bestseller
Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijr Labarai 👇