Gobara Ta Tashi a Majalisar Dokokin Jihar Katsina Ta Lalata Abubuwa da Dama

 Gobara Ta Tashi a Majalisar Dokokin Jihar Katsina Ta Lalata Abubuwa da Dama

Best Seller Channel 

 Best Seller Channel 

Best seller Channel ta rawaito wasu ofisoshi a harabar majalisar dokokin jihar Katsina sun kone kurmus a daren Lahadi. 

Ofisoshin da abin ya shafa sun hada da na magatakardar majalisar da na majalisar dokokin. 

Kakakin majalisar, Tasi’u Magarin, ya tabbatar wa Jaridar PUNCH faruwar lamarin a ranar Talata. 

Best Seller Channel 

Tasiu ya bayyana cewa gobarar ta tashi ne da misalin karfe 6:30 na yammacin ranar Lahadi, inda ya kara da cewa daukar matakin da jami’an hukumar kashe gobara ta jihar suka yi a kan lokaci ya hana ta yaduwa fiye da ofisoshin da abin ya shafa. 

Ya Kara da cewa, a ranar Laraba ne za a kafa wani kwamiti da zai binciki yadda lamarin ya faru da sauran bayanai. 

Majiyoyi sun bayyana cewa gobarar ta shafe sama da sa’o’i uku tana ci kafin daga bisani ‘yan kwana-kwana su kashe ta. 

Best Seller Channel 

Wata majiya ta ce, “Gobarar ta tashi ne da misalin karfe 6:30 na yammacin ranar Lahadi, bisa ga dukkan alamu wutar lantarki a daya daga cikin ofisoshin da abin ya shafa. 

‘Yan kwana-kwana da aka kira don kashe ta sun shafe kusan sa’o’i hudu a nan kafin daga bisani a kashe wutar da daddare. 

Kayayyakin da aka lalata sun hada da na’urorin lantarki, daki da kuma takardu.

Best Seller Channel 

 Jami’an majalisar sun takaita zirga-zirga zuwa ofisoshin da abin ya shafa a ranar Talata. 

Daya daga cikin jami’an ya ce, “An umurce mu da kada mu bari a dauki hotuna ko bidiyo na ofisoshin da abin ya shafa.” 

Ana sa ran majalisar da ke hutu za ta koma zamanta a watan Fabrairu. 

 Za a iya tunawa cewa wasu sassan majalisar sun yi aman wuta a watan Afrilun 2021.

Slide Up
x