Gwamna Abba Kabir Yusuf na jihar Kano ya amince da sayan taki na kimanin Naira biliyan 5.07 domin tallafawa kananan manoma a jihar.
Alfijir labarai ta ruwaito wannan yunkuri na da nufin saukaka wadatar abinci a matsayin sabon tsarin ci gaban noma a jihar.
A cewar wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sanusi Bature Dawakin-Tofa ya fitar a Kano a yau Talata, an ba da amincewar ne yayin taron majalisar zartarwa ta jiha karo na 15, SEC.
“Za a raba takin ne a fadin kananan hukumomi 44 domin tallafa wa manoma musamman na karkara domin kara yawan amfanin gona a kakar damina ta 2024,” inji shi.
Ya bayyana cewa za a sayar wa manoman takin ne a kan farashi mai rahusa, wanda hakan ke nuna aniyar gwamnan na samar da kayan amfanin gona masu inganci da araha.
Wannan matakin ya biyo bayan siyan hatsi na biliyoyin naira a baya da gwamnan ya yi, inda aka raba wa marasa galihu a jihar domin rage raɗaɗi.
Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a
https://twitter.com/Musabestseller?s=09
https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165
https://www.threads.net/@alfijirlabarai
https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12
https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag
Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijr Labarai 👇👇
https://chat.whatsapp.com/ELQRQyq1zGn7zpAVP8DwNj