Gwamnatin Kano Ta Amince Da  Fitar Da Naira N97m, Domin  Biyan Diyyar Gidajen Da  Za’a Gina Ofishin Yan Sanda A Dorayi

FB IMG 1720071046360

Gwamnatin Jihar Kano ta  Amince Da fitar Da kudin fiye Da Naira Miliyan Casa’in da bakwai domin  biyan Wadanda Suka Mallaki Gidaje a  wurin da  Za’a gina Ofishin  Yan Sanda a Unguwar Dorayi Karama dake karamar hukumar Gwale.

Alfijir labarai ta ruwaito shugaban rikon karamar hukumar Gwale,  Alhaji Abubakar Mu’azu Yusuf Mojo ne ya bayyana hakan a jiya Laraba lokacin da yake ganawa da manema labarai.

Mojo, Yace  tini aka Biya mamallakan  wadanda Gidaje kudaden su, kuma nan bada Jimawa ba Za’a Fara  aikin Gina Ofishin Yan Sandan, domin kawo karshen matsalar rashin tsaro  tare da tabbatar zaman lafiya a yankin.

Shugaban karamar hukumar Yace, sun yi nasarar gyara motocin Jami’an Tsaro a karamar hukumar ta  Gwale duk da nufin inganta harkokin Tsaro a yankin.

Ya godewa Gwamnan Abba Kabir Yusuf da mataimakinsa Kwamared Aminu Abdulsalam Gwarzo bisa yadda suke nuna kishin karamar hukumar ta Gwale dama Jihar Kano baki daya.

Shugaban ya Kuma yabawa shugabannin jami’an tsaron yankin, bisa irin Jajircewarsu,  yana mai Kira ga Alummar karamar hukumar su bada hadin kai da goyan baya ga jami’an tsaron  domin cimma nasara.

Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a

https://twitter.com/Musabestseller?s=09

https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165

https://www.threads.net/@alfijirlabarai

https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12

https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag

Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijr Labarai 👇👇

https://chat.whatsapp.com/ELQRQyq1zGn7zpAVP8DwNj

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *