Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Ranaku 2 A Matsayin Hutu 

FB IMG 1710375660100

Gwamnatin Tarayya ta bayyana ranar 29 ga Maris da 1 ga Afrilu a matsayin ranakun hutun bukukuwan Good Friday da Easter Monday na bana.

Alfijir labarai ta rawaito Ministan cikin gida, Olubunmi Tunji-Ojo, shi ne ya bayyana haka a madadin Gwamnatin Tarayya a ranar Laraba.

Ya bayyana hakan ne a ciki wata sanarwa mai ɗauke da sa hannun Babbar Sakatariyar Ma’aikatar, Aishetu Ndayako.

Tunji-ojo ya yi amfani da wannan dama wajen kira ga mabiya addinin Kirista da ma ‘yan ƙasa baki ɗaya kan a yi koyi da karantarwa Yesu kamar yadda ya nunar a halin rayuwarsa.

Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a

https://twitter.com/Musabestseller?s=09

https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165

https://www.threads.net/@alfijirlabarai

https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12

https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag

Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijir Labarai 👇

https://chat.whatsapp.com/CJ2q8cmhhOxFY6OEgwV5vk

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *