Hukumar Kula Da Filayen Jiragen Sama Ta Najeriya FAAN Ta Rufe Filin Jirgin Saman Lagos

Alfijr ta rawaito Hukumar kula da filayen jiragen sama ta Najeriya (FAAN) ta ce an rufe titin jirgin da ke filin jirgin saman Murtala Muhammed (MMIA) da ke Ikeja a jihar Legas na tsawon makonni takwas.

A cikin wani sakon twitter a ranar Litinin, Hukumar ta sake nanata kudurinta na aminci, tsaro da kimarta.

Za a yi amfani da hanyar taksi B-18L don duk ayyukan jirgin,” in ji shi.

Sanarwar ta kara da cewar, ana sanar da jama’a cewa an rufe titin jirgin sama mai lamba 18R/36L na filin jirgin saman Murtala Muhammed Int’l, Legas na tsawon makonni 8 don gudanar da aikin gyare gyare.

Za a yi amfani da hanyar taksi B-18L don duk ayyukan jirgin.

FAAN, ta himmatu wajen bin ka’idojinta..Lafiya, Tsaro da Jin kai. In Ji sanarwar

Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a

Facebook.   Alfijr Labarai
YouTube.     Best Seller Channel
Twitter.        @Musabestseller
Instagram.  @musa_bestseller

Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijr Labarai 

https://chat.whatsapp.com/G1wNveF9mGU7jec5mWhFvZ

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *